Rahotanni sun bayyana cewa yawancin wadanda aka hallaka a kusa da birnin Deir al-Zour mata ne da kananan yara da kuma tsofaffi.
Kungiyar da ke ikirarin kafa daular musulunci a kasashen Iraqi da Syria wato IS, ta bullo da sabbin hanyoyin kai hare-hare a gundumomin da gwamnatin Syria ke iko da su da kuma birane.
Wasu rahotannin sun ce an hallaka dakarun gwamnati da fararen hula a wasu biranen kasar.
A bangare guda kuma Majalisar Dinkin Duniya ta ce akwai fargabar mutane 200,000 na fuskantar barazanar karancin abinci a Syria.288